INA SOJOJIN LEBANON SUKE BAYAN KNUTSEN ISRA'ILA?

 Ina sojojin Lebanon suke bayan kutsen Isra'ila?



Yaƙin da ake gwabzawa tsakanin Isra'ila da Hezbollah, matsala ce a kan abubuwa guda biyu da suka ƙi ci suka ƙi cinyewa na kusan shekara 40.


Isra'ila ta ce ba za ta gaji ba sai ta ga bayan barazanar da Hezbollah ta Lebanon, ita kuma Hezbollah tana ci gaba da kai hare-hare a wasu yankunan Isra'ila.


Kimanin wata 11 da suka gabata, yaƙin a tsakanin ɓangarorin guda biyu na ta ƙara ta'azzara.


Yanzu da Isra'ila ta ƙaddamar da kutsawa cikin Lebanon ta ƙasa a karon farko tun bayan shekarar 2006, mutane da dama tambaya suke yi wai ina sojojin ƙasan Lebanon suke ne, kuma me suke yi domin hana yiwuwar hakan, musamman ganin irin tasirin da hakan zai yi a yankin baki ɗaya.

Post a Comment


Yi Comment domin ka bayyana ra'ayinka akan wannan labarin anan akasa

Previous Post Next Post