ZANGA ZANGAR A NIGERIA: 'HAR CKIN GIDA SUKA YO HARBI SUKA KASHEMIN DANA...

 


Zanga-zanga a Najeriya: 'Har cikin gida suka yo harbi suka kashe ɗana'

Iyalan matashi Isma'il Muhammad sun bayyana kisan da ake zargin sojoji da yi wa ɗansu da "ba zato ba tsammani" yayin zanga-zanga kan tsadar rayuwa a unguwar Samaru da ke garin Zariya na jihar Kaduna.


Ya zuwa safiyar Talata, lokacin da BBC ta tattauna da Muhammad Hussain - wanda shi ne mahaifin Isma'il - bai gama farfaɗowa daga kaɗuwar rasuwar ɗan nasa mai shekara 16 ba.


"Harbi na farko da (soja) ya yi, ya same shi a wuya, ya sake yin harbi na biyu ya same shi a baya, nan take Isma'il ya mutu," in ji mahaifin Isma'il.


Wannan ɗaya ne daga cikin labaran da ke fitowa na mutanen da suka rasa rayukansu a Najeriya tun bayan fara zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa da manufofin gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu.


Sai dai akasin sauran kashe-kashe da ake zargin jami'an tsaro da aikatawa a lokacin zanga-zangar, a wannan karo sojojin Najeriya sun ɗauki alhakin kisan, inda suka fitar da sanarwa suna bayyana takaici kan faruwar lamarin.

@Ma'asumah Nigerian News update

Post a Comment


Yi Comment domin ka bayyana ra'ayinka akan wannan labarin anan akasa

Previous Post Next Post