KOFAR GIDAN MUHAMMAD HUSAINI INDA ZA'A IYA GANIN RAMIN DA HARSASHI YA BULA..



 Ƙofar gidan Muhammad Hussaini inda za a iya ganin ramin da harsashi ya ɓula

Tun bayan fara zanga-zangar a ranar 1 ga watan Agusta, lamarin ya rikiɗe zuwa tarzoma a jihohi da dama na arewacin ƙasar.


Wannan ne ma ya haifar da sanya dokar hana fita a jihohi bakwai; wato Borno, Kano, Yobe, Jigawa, Katsina, Filato, Kaduna.


A jihar Kaduna, an sanya dokar ce a babban birnin jihar da kuma Zariya, garin da aka bayyana cewa zanga-zangar ta so ta ƙazance.


Hotunan bidiyo da aka riƙa yadawa a intanet sun nuna yadda dandazon mutane suka mamaye tituna a garin na Zariya, yayin da wani bidiyon ya nuna wasu mutane na fasa wurin ajiye abinci, wanda aka ce a birnin na Zariya ne.


Sai dai a cewar mahaifin marigayi Isma'il, duk da zanga-zangar da ta wakana a Zariya har aka sanya dokar hana fita ta sa'a 24, babu wata tarzoma da ta tashi a unguwar Samaru.


Ya ce: "Babu wata zanga-zanga a Samaru, gaba ɗaya mu ba a samu zanga-zanga a Samaru ba tun bayan da aka fara wannan abu (zanga-zanga).


Wannan tsautsayi ya faɗa kan Isma'il ne a daidai lokacin da ya kammala karatunsa na ƙaramar sakandare, yana shirin zuwa aji ɗaya (SS I) na babbar makarantar sakandare.


A lokacin da yake bayyana halin ɗan nasa, Muhammad Hussain ya ce "yaron kirki ne, ba shi da hayaniya, ba a faɗa da shi kuma yana da saurin kuka".

@Ma'sumah Nigerian News update

Post a Comment


Yi Comment domin ka bayyana ra'ayinka akan wannan labarin anan akasa

Previous Post Next Post