Sudan Tana Bukatar Yarjejeniya Kan Yadda Za’a Amfana Da Ruwan Nilu Ba Yaki Ba

   2021-04-18 

Shugaban majalisar koli ta gwamnatin rikon kwarya ta kasar Sudan

Abdel Fattah Al-Burhan ya bayyana cewa gwamnatin kasar Sudan tana

son fahintar juna tsakanin kasashen wadanda kogin Nilu ta ratsa a

kasashensu, su rattaba hannu kan yarjejeniya wacce zata lamuncewa

ko wace kasa kasonta na ruwan Nilu.

Jaridar Egypt Daily ta kasar Masar ta nakalto Al-Burhan yana fadar

haka a wata hira da ta hada shi da tashar talabijin ta Al-Arabiyya a

ranar jumma’an da ta gabata. Ya kuma kara da cewa, gwamnatin Sudan

tana bukatar Habasha ta janye sojojinta daga bangaren kasar Sudan da

take mamaye da su.

Banda haka Al-Buryan yayi magana kan wasu al-amura da suka shafi

kasarsa wadanda suka hada da rikicin madatsar ruwa ta Renaissance

ta kasar Habasha da rikikin yankin Darfur da kuma matsalolin tattalin

arziki wanda kasar take fama da su.


Source: BIN MUHAMMAD PRESS

WHATSAPP GROUP

08032147367

Post a Comment


Yi Comment domin ka bayyana ra'ayinka akan wannan labarin anan akasa

Previous Post Next Post