Rikice-rikice Na Kawo Tarnaki Ga Ayyukan Jin Kai A Jihar Borno


 2021-04-18 


MDD ta ce rikice-rikice tsakanin kungiyoyin ‘yan ta’adda da sojojin

gwamnati a jihar Borno dake arewa maso gabashin Najeriya, na yi wa

ayyukan jin kai a jihar tarnaki.

Kakakin Sakatare Janar na MDD Antonio Guterres, ya ce ma’aikatan jin

kai na MDD na ci gaba da samun rahotanni masu tayar da hankali

dangane da arangamar da ake tsakanin ‘yan ta’adda da sojojin kasar a

garin Damasak na jihar.

Stephane Dujarric, Ya kara da cewa, a makon da ya gabata ma, an kai

hari kan kadarorin ma’aikatan jin kai a Damasak, inda aka lalata

ofisoshin kungiyoyin ayyukan jin kai a kalla 5, da tarin motocinsu, da

wajen adana kayayyaki na tafi da gidanka, da tankunan ruwa, da wata

cibiyar kula da lafiya, ta kula da masu fama da tamowa. An kuma samu

karin rahotannin rikice-rikice a wannan makon.

Mista Dujarric, ya yi gargadin cewa, wadannan hare-hare za su yi tasiri

kan ayyukan jin kai da kariyar da ake ba kusan ‘yan gudun hijira 9,000

da wasu mutane 76,000 na yankin dake ba ‘yan gudun hijirar mafaka.

024


Source: BIN MUHAMMAD PRESS

WHATSAPP GROUP

08032147367

Post a Comment


Yi Comment domin ka bayyana ra'ayinka akan wannan labarin anan akasa

Previous Post Next Post