A yau Litinin aka cigaba da sauraren karar da Gwamnatin Kaduna ta shigar da nufin tuhumar Sheikh Zakzaky da matarsa Malama Zeenat, anyi Zaman Kotu ga kuma yadda abin ya kasance.
Daga Wakilin Shafin Ma'asumah --Idishia Jos.
Yau ma Allah ya sake dawo da mu babbar kotun jihar Kaduna don ci gaba da shari'ar da Gwamnati Kaduna ta shigar kan jagoran Harkar Musulunci Shaikh Zakzaky da Matarsa.
Yanzu haka Lauyoyin gwamnati da na Shaikh Zakzaky duk sun iso kotu. Shaikh Zakzaky da Matarsa Malam Zeenat sun iso kotu. Ana jiran shigowar alkali ne din fara shari'ar.
Alkali ya shigo kotu. An kira qara Lauyoyi sun gabatar da kansu. Batista Sadau Garba ya nemi amincewar kotu kan Abubakar Marshall ya jagoranci zaman. Alkali ya amince.
Abubakar Marshall ya shaidawa kotu rashin hakartar Femi Falana SAN. Ya kuma nemi afuwar kotu kan wannan.
Abubakar Marshall ya shaida wa kotu cewa a zaman da ta yi na baya, ta baiwa gidan Yari umarnin su bar Likitocin Malam su duba su. Amma gidan Yari sun ki bin wannan umarnin duk da cewa a mika musu takardar umarnin da kotu ta bayar.
Ya ce hukunar gidan Yari din sun bayyana cewa wannan odar da kotu ta bayar ba cewa ta yi Likitoci su yiwa su Malam aiki ba. Wai kotu na nufin Likitocin su Kalli Malam ne a matsayin kallo na idanu. Don haka ya shaida wa kotu cewa tun daga wannan ranar zuwa yau ba a yi wa wadanda ake kara aikin komai ba dangane da hakin rashin lafiyar da suke fama da ita. Ya ce lallai suna bukatar kukawar gaggawa daga Likitocin su. Ya bayyana cewa ranar Juma'ar da ta gabata sai da almajiran Malam suka yi yajin cin abinci a gidan Yari don yin Allah wadai da wannan hali na hukumar gidan Yari din. Hakan ce ya tilasta hukumar gifan Yari din barin a debi jinin su Malam don yin Text.
Abubakar Marshall ya ci gaba da shaida wa kotu cewa Malam da Malama na da yancin a bar Likitocinsu su duba su. Ya ce duk yunqurin da aka yi don kai su Malam in da za a yi musu Text, ya ci tura, saboda hukumar gidan Yari ta qi bin umarnin kotu.
Don haka ya nemi kotu da ta tilasta hukumar gidan Yari da su bar Malam da Malama likitocin su su yi musu aiki. Ya ce domin waccan odar da kotu ta bayar cewa ta yi wai Likitocin Malam su zo su ganshi fa ido su koma ba Wai su yi masa aiki ba.
Don haka ya cemi kotu ta sake ba da wata odar na cewa a bar Likitocinsu su yi musu aiki. Ya ce yanzu haka Malama Zeenat jini ke zuba a hancinta da bakinta. Ya ce wannan na tabbatar da cewa wadanda ake kara na cikin tsananin rashin lafiya. Ya ce shima Malam yanzu jininsa ya kusa kaiwa 200. Ya ce wanda ke wannan halin yana bukatar kukawar gaggawa daga Likitocin sa
Lauyan gwamnati, Bayero Dari ya bayyana cewa sun bi umarnin kotu. Domin gidan Yari sun nemi a ba su sunayen likitocin da za su zo Kuma an ba su ta hannun chamber din Sadau Garba. Kuma hukumar gidan Yari sun rubuta wa gwamnati, in da suma suka ba da Likita daya. Likitoci suka zama hudu. Likitocin Malam 3 daga asibitin koyarwa na Aminu Kano da kuma 1 daga jihar Kaduna.
Kuma dukkansu 4 sun je sun duba wadanda ake kara. Dari ya bayyana cewa yana da dukkan takardun da suke tabbatar da abin da ya fada.
Ya ce in da aka sami matsala shi ne su Likitocin Malam sun je dole ne a fitar da wadanda ake kara zuwa wani asibiti don duba su. Su kuma hukumar gidan Yari sun qi amincewa da hakan. In da suka ce dole sai dai a yi komai a gidan Yari din.
Alkali ya bayyana cewa bai ji dadin yadda aka kasa magance wannan matsalar ba. Ya ce ba yada za a yi a hana Wanda ake ka qara kukawar Likitoci.
Ya ce dole su ga shugaban gidan Yari din magance wannan matsala. Ya ce tambayi Abubakar Marshall cewa zai koma Abuja ne ko zai tsaya a Kaduna? Marshall ya ce zai tsaya saboda a magance wannan matsala.
Alkali ya aika a kira mas shugaban gidan Yari don ya fada masa dalilin kin bin umarnin kotu.
An daga Shari'ar Sai zuwa 23-24 March 2020
Daga Shafin Ma'asumah Nigerian News Updates.
Daga Wakilin Shafin Ma'asumah --Idishia Jos.
Yau ma Allah ya sake dawo da mu babbar kotun jihar Kaduna don ci gaba da shari'ar da Gwamnati Kaduna ta shigar kan jagoran Harkar Musulunci Shaikh Zakzaky da Matarsa.
Yanzu haka Lauyoyin gwamnati da na Shaikh Zakzaky duk sun iso kotu. Shaikh Zakzaky da Matarsa Malam Zeenat sun iso kotu. Ana jiran shigowar alkali ne din fara shari'ar.
Danna Jan Rubutun Domin samun rubucenmu a Facebook Yanzu: -Ma`asumah Nigeria 🇳🇬 news 📰 update kayi like bayan ka shiga
Kamar kullum AU Tumburkai ne zai kasance tare da ku kai tsaye daga kotun.Alkali ya shigo kotu. An kira qara Lauyoyi sun gabatar da kansu. Batista Sadau Garba ya nemi amincewar kotu kan Abubakar Marshall ya jagoranci zaman. Alkali ya amince.
Abubakar Marshall ya shaidawa kotu rashin hakartar Femi Falana SAN. Ya kuma nemi afuwar kotu kan wannan.
Abubakar Marshall ya shaida wa kotu cewa a zaman da ta yi na baya, ta baiwa gidan Yari umarnin su bar Likitocin Malam su duba su. Amma gidan Yari sun ki bin wannan umarnin duk da cewa a mika musu takardar umarnin da kotu ta bayar.
Ya ce hukunar gidan Yari din sun bayyana cewa wannan odar da kotu ta bayar ba cewa ta yi Likitoci su yiwa su Malam aiki ba. Wai kotu na nufin Likitocin su Kalli Malam ne a matsayin kallo na idanu. Don haka ya shaida wa kotu cewa tun daga wannan ranar zuwa yau ba a yi wa wadanda ake kara aikin komai ba dangane da hakin rashin lafiyar da suke fama da ita. Ya ce lallai suna bukatar kukawar gaggawa daga Likitocin su. Ya bayyana cewa ranar Juma'ar da ta gabata sai da almajiran Malam suka yi yajin cin abinci a gidan Yari don yin Allah wadai da wannan hali na hukumar gidan Yari din. Hakan ce ya tilasta hukumar gifan Yari din barin a debi jinin su Malam don yin Text.
Abubakar Marshall ya ci gaba da shaida wa kotu cewa Malam da Malama na da yancin a bar Likitocinsu su duba su. Ya ce duk yunqurin da aka yi don kai su Malam in da za a yi musu Text, ya ci tura, saboda hukumar gidan Yari ta qi bin umarnin kotu.
Don haka ya nemi kotu da ta tilasta hukumar gidan Yari da su bar Malam da Malama likitocin su su yi musu aiki. Ya ce domin waccan odar da kotu ta bayar cewa ta yi wai Likitocin Malam su zo su ganshi fa ido su koma ba Wai su yi masa aiki ba.
Don haka ya cemi kotu ta sake ba da wata odar na cewa a bar Likitocinsu su yi musu aiki. Ya ce yanzu haka Malama Zeenat jini ke zuba a hancinta da bakinta. Ya ce wannan na tabbatar da cewa wadanda ake kara na cikin tsananin rashin lafiya. Ya ce shima Malam yanzu jininsa ya kusa kaiwa 200. Ya ce wanda ke wannan halin yana bukatar kukawar gaggawa daga Likitocin sa
Lauyan gwamnati, Bayero Dari ya bayyana cewa sun bi umarnin kotu. Domin gidan Yari sun nemi a ba su sunayen likitocin da za su zo Kuma an ba su ta hannun chamber din Sadau Garba. Kuma hukumar gidan Yari sun rubuta wa gwamnati, in da suma suka ba da Likita daya. Likitoci suka zama hudu. Likitocin Malam 3 daga asibitin koyarwa na Aminu Kano da kuma 1 daga jihar Kaduna.
Kuma dukkansu 4 sun je sun duba wadanda ake kara. Dari ya bayyana cewa yana da dukkan takardun da suke tabbatar da abin da ya fada.
Ya ce in da aka sami matsala shi ne su Likitocin Malam sun je dole ne a fitar da wadanda ake kara zuwa wani asibiti don duba su. Su kuma hukumar gidan Yari sun qi amincewa da hakan. In da suka ce dole sai dai a yi komai a gidan Yari din.
Alkali ya bayyana cewa bai ji dadin yadda aka kasa magance wannan matsalar ba. Ya ce ba yada za a yi a hana Wanda ake ka qara kukawar Likitoci.
Ya ce dole su ga shugaban gidan Yari din magance wannan matsala. Ya ce tambayi Abubakar Marshall cewa zai koma Abuja ne ko zai tsaya a Kaduna? Marshall ya ce zai tsaya saboda a magance wannan matsala.
Alkali ya aika a kira mas shugaban gidan Yari don ya fada masa dalilin kin bin umarnin kotu.
Danna Jan Rubutun Domin samun rubucenmu a Facebook Yanzu: -Ma`asumah Nigeria 🇳🇬 news 📰 update kayi like bayan ka shiga
Kotu ta dage zama sai 12 na rana, A halin da ake ciki Lauyoyi da Shugaban gidan Yari da kuma Likitan gidan Yari da kuma Malam da Malama duk suna chamber suna ganawa da Alkali. Bisa dukkan alamu a Chamber za a gaba zaman yau.An daga Shari'ar Sai zuwa 23-24 March 2020
Daga Shafin Ma'asumah Nigerian News Updates.
Tags:
Labaran Duniya