Shaheeda Alhasan| Ko Yanzu Idan Mijina Ya dawo Zamu Zauna!!!





Cewar Matar Shaheed Alhaji Ibrahim Ahmad MD alheri block

🇮🇪Ma'asumah Nigerian News Update

Firar dasukai da wakilinmu

MJ'Matashi Ibrahim

WAKILINMU
Sunana MJ Matashi Ibrahim kozan iya sanin sunan malamar

SHAHEEDA
Sunana:- Shaheeda Alhassan

WAKILINMU
Kina wanne garine da zama

SHAHEEDA
Bauchi(misau)


WAKILINMU
 zakikai shekara nawa yanzu

SHAHEEDA
Shekarata 22

WAKILINMU
Kina da aure

SHAHEEDA
Eh amma mijina yayi shahada a Zaria 2015

WAKILINMU
Amma zakukai shekara nawa da aure yayi shahada

SHAHEEDA
Watanmu Bakwai

WAKILINMU
Kafin kuyi aure dashi yana da wata matar

SHAHEEDA
Eh, yana da mata daya da yara (7)

WAKILINMU
Bayan kunyi aure wanna darasi kika dauka dangane da zama dashi dakuma ita abokiyar zaman naki dama yaranta

SHAHEEDA
To a zamana da Mijina wato Shahid, Zama mukayi wata bakwai Amma tamkar munyi shekara bakwai Shi wato tun bayanda mukayi aure Sbd irin tausayinsa garemu Kyautatawarsa, Ibadarsa, Kyauta, Hakuri Ga girmamawa hatta ga na kasa dashi Wannan dalilin yasa wasu lokuta nakan Kira Shi da 'Shahid.

Idan zaka cutar dashi sau nawa wlh bazai tamka ba Amma abinda ya shafi Addini bai daukesa da wasa ba Akwai wata kauna boyayya wadda yake ma Abba (H)  Wadda bansan ya zan misalta a fahimta ba Wata Rana sai nayi mafarki, Ana program haka to Su ABBA (H) sune suke jawabai sai muka iso ni dashi a makare Sai muka fito a motansa muka shigo wajen program din ABBA na jawabi, sai na wuce bangaren sisters Wallahi billahi sai ABBA suka dakata da jawabin suka zo suka nuna masa inda zai zauna.

WAKILINMU
Agefe gudu yaza mantakewarki takama keda dayar matar tasa

SHAHEEDA
Dayake ba gida daya muke ba Dan haka bamu zauna tare ba sai bayan da akai waqi'a

Akwai kauna tsakanina da yaransa Mun shaku da diyarsa wacce ita ce auta ya tafi lokacin tana rarrafe Sunanta Sukaina, Ina matukar sonta, akwai shakuwa wadda Allah ya kimsa tsakanina da ita sosai

Ina kaunar mijina yana kaunata Azzaluman(Sad) Mamuguntan najeriya suka rabani dashi, Bazamu yafe ba da sannu sai mun dauki fansarku Habeybeee na

WAKILINMU
Amma idan akace miki mijinki yadawo ya zakiji aranki

SHAHEEDA
Bazan misalta ba  Amma lallai sabuwar kyauta ce daga Allah Amma tabbas hakan shine farin cikina

WAKILINMU
Amma idan kika samu wani mijin zaki aure ko kwa kin hakura

SHAHEEDA
To wannan nufin Allah ne Amma idan a so nane na samu nawa rabon na riski mijina

WAKILINMU
To wanne kira zaki ga yan uwa mata wadand suka smu jarabawa irin taki

SHAHEEDA
To kirana garesu shine Mu sani kuma muji cewa yanzu ne zamu fara ita wannan gwagwarmaya dinKashe mazajenmu baisa mana rauni ba Face ya kara Mana izza da kumaji akan ita wannan tafiya din Yadda muke alfahari da mazajenmu kan hanyarda suka tafi to muna fatan suma mazajenmu suyi alfahari damu akan abinda suka barmu akai har zuwa ranarda zamu riskesu

WAKILINMU
Amma haryanzu kema kina da burin kitafi akan abin da yatafi

SHAHEEDA
Kwarai kuwa Shine babban burina tun bayan tafiyar ban saurara ba Ba Kuma zan tsagaita ba har sai mun cimma hadafi

WAKILINMU
Daga karshe wanne kira zaki gayan uwa

SHAHEEDA
Babban kirana abinda yafi damuna Muji tsoron Allah mu hada kanmu, domin rarrabar kanmu shine babban makamin jahiliyya da zasu yakemu Muyi aiki da iklasi musamu yardar Allah Mu dake mu jure hanyar akwai wahala Amma dadinta yana gaba

Fatan Allah ya tabbatar damu ya bamu sabaty Allah ya tausaya Mana Yaba ma bayinsa Lafiya ABBA da UMMA ZEENA Ya kwato Mana su dg hannun miyagun bayi

Allah ya karawa addininsa kariya ta musamman.


WAKILINMU
Muna godiya sosai dafatan koda gaba munkara nemanki zamusamu hadinkai kamar yau.

SHAHEEDA
Elahee Ajab nima ngd

Post a Comment


Yi Comment domin ka bayyana ra'ayinka akan wannan labarin anan akasa

Previous Post Next Post