Sayyid Badamasi Yakub yayi kira da a rika tunawa da Malam haruna Abbas

Sayyeed Badamasi Yaqub Zakzaky yayi kira ga yan uwa almajiran Sayyeed Zakzaky (h) da su rinka tunawa da dan uwan da azzalumai suka dade suna zalunta .
Sayyeed Badamasi Yaqub Zakzaky yace kasar Isra’ila ce ke tsare da Malam Haruna Abbas tun kafin wannan waki’ar da muke ciki. Don haka yayi kira ga yan uwa da su sanya Mal Haruna Abbas a cikin addu’oinsu.

Sayyeed Badamasi Yaqub Zakzaky yayi wannan kira ne a Jannati Dari rahama Dembo Zaria, lokacin jana’izar dan uwan da yayi Shahada jiya a wurin Muzahara a garin Kaduna.

A karshe Sayyeed Badamasi yayi addu’ar Allah ya sanya jinanen wadannan shahidai ya zamo sanadiyar rayuwar bishiyar wannan harka. Kuma ya roki Allah ya tabbatar da addini albarkacin jinanen wadannan Shahidai namu.
ZAINILABIDINA AHMAD SULEIMAN

My Name is Zainilabidina Ahmad Suleiman Chief Executive Officer CEO Bz News 24/7. Famous Blogger| Developer | Programmer| Journalist| Consultant |Publisher |. Contact bzglobalservice@post.com Whatsapp+2348133888333

Post a Comment


Yi Comment domin ka bayyana ra'ayinka akan wannan labarin anan akasa

Previous Post Next Post