Ga Saqo Nan, In Za Ka bi, Kabi..!!!



👆🏽------------------------- 👇🏽
--Inji jagoran gaskiya [Sayyid Ibrahim Alzakzaky]

"Wato a taqaice abin da nake cewa, ‘destiny’ din al’ummar nan yana 
hannunmu ne, kuma ba zai taba yiwuwa kana tunanin wai gyaran Allah 
kawai a wayi gari a ga an gyaru ba. Gyaran Allah shi ne me kake so 
Allah ya yi maka? Ya aiko da wane Annabi? Ya riga ya aiko.

 Ko ya 
sauqar da wane Alqur’ani? Ya riga ya sauqar.

 Ba abin da zai yi maka 
illa ga saqon nan, in za ka bi ka bi, in ba za ka bi ba kuma ya rage maka, 
a hadu a ranar hisabi. 

To, ni yanzu na ga kamar mutane sun yi saranda ga halin da suka 
sami kansu ne, ana jiran kawai a yi ta tafiya haka nan. Kuma kullum 
abubuwa sai qara tabarbarewa suke yi da lalacewa. In ka ga wannan 
nau’in lalacewa ya fito, sai ka ga na kashegari ya fi shi muni. Sai ka ga 
wani ya sake kunno kai, shi kuma ya fi na jiya, kuma haka ake ta tafiya 
ana dai zaune haka nan kawai. 
Abin da nake cewa in wadansu mutane in za su zama ma’azurai, 
musulmi ba shi da uzuri, don shi tsiransa na hannunsa. Shi Allah Ta’ala
ya fifita da shiriya, sai ya ajiye waje guda. Ba wata mafita gare mu illa 
mu san cewa mune da kanmu za mu yi, ba kuma jiran wani za mu yi ba. 
Mune da kanmu, kuma al’marin yana hannunmu ne!�

👇🏽------------------------👇🏽
Ma'asumah Nigeria 🇳🇬 News Update,  [Filin jagoran gaskiya]
Wakilinmu:
             👇🏽
Mahadi Tukur Almizan

Post a Comment


Yi Comment domin ka bayyana ra'ayinka akan wannan labarin anan akasa

Previous Post Next Post